bbc.co.uk navigation

Jama'a basu fito sosai ba a zaben Ivory Coast

An sabunta: 11 ga Disamba, 2011 - An wallafa a 15:27 GMT

An rufe rumfunan zabe a yinin farko na zaben 'yan majalisar dokoki a Ivory Coast, wanda shi ne zaben farko tun bayan zaben shugaban kasar da ya haddasa rikicin siyasar kasar.

Jam'iyyar Laurent Gbagbo, tsohon shugaban kasar tana kaurace wa zaben.

Kin saukarsa daga kan mulki bayan zaben shugaban kasa a bara ya jawo mummunan zubar da jini a kasar.

'yan jami'yyar sun yi kukan ana musguna masu, kuma hukumomin zabe suna fifita jam'iyyar Shugaba Alassane Ouattara.

An dai kai Mr. Gbagbo kotun hukunta laifukan yaki da ke Hague don fuskantar tuhumar aikata laifukan cin zarafin bil'adama.

Daruruwan magoya bayansa ne dai suka yi zanga-zanga a harabar kotun don nuna adawar su da shari'ar da ake yi masa.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.