
'Yan sandan Najeriya
Rundunar 'yan sandan Najeriya ta kammala wani taro na kwanaki biyu, game da batun tabarbarewar tsaro a kasar, ba tare da ta yi bayyani akan abubuwan da ta cimmawa ba.
An yi tsammanin a wajen taron za a tabo batun kungiyar nan ta Boko Haram, wadda ake zargi da kai hare hare da kuma dasa bama bamai.
To amma babu inda aka ambaci sunan kungiyar ta Boko Haram a wajen taron 'yan sandan.
A makon da ya gabata ne kungiyar ta Boko Haram, wadda kuma ake kira Ahlus Sunna Lil-da'awati wal Jihad, ta kai harin bam a hedkwatar rundunar 'yan sandan ta kasa dake Abuja.
An sami hasarar rayuka da dukiya a lokacin harin.