Hotuna: yajin aikin 'yan kwadago a Najeriya
-
A jihar Kaduna tsohon gwamnan jihar a lokacin jamhuriya ta biyu Alhaji Balarabe Musa da kuma dan fafutukar kare hakkin bil'adama Shehu Sani, su ne suke jagorantar dubun-dubatar masu zanga-zanga. Yayin da a Kano manyan malaman jami'a suka fito domin baiwa masu zanga-zangar goyon baya. Hoto Nura Muhammad Ringim








































