Ra'ayi Riga: Shin akwai bukatar guguwar sauyi a Afrika?

An sabunta: 27 ga Janairu, 2012 - An wallafa a 21:26 GMT

Garmaho

A daidai lokacin da ake bukukuwan tunawa da boren da aka yi a kasashen Tunisia da Masar wanda ya kifar da gwamnatocin kasar, sannan ya haifar da bore a wasu kasashen Larabawa: Tambayar ita ce ko za a sami makamancin wannan boren a kasashen Afrika?

Sauraremp3

Ba ka da manhajar flash player da ta dace

Kunna wannan da wata manhajar ta daban

Ra'ayi Riga: Shin akwai bukatar guguwar sauyi a Afrika?

Jama'a da dama na nuna adawarsu da gwamnatoci da dama a Afrika


A daidai lokacin da ake bukukuwan tunawa da boren da aka yi a kasashen Tunisia da Masar wanda ya kifar da gwamnatocin kasar, sannan ya haifar da bore a wasu kasashen Larabawa: Tambayar ita ce ko za a sami makamancin wannan boren a kasashen Afrika?

An kifar da gwamnatoci, masu mulkin kama-karya sun sha kasa, an watsa boren a gidajen talabijin ta hanyar da ba a taba tsammani ba watanni 12 da suka gabata.

Nahiyar Afrika na daga cikin sassan duniya da ke da shugabannin da suka dade suna mulkin kama-karya - kuma wannan shi ne abinda mazauna kasashen Larabawan ke adawa da shi.

Tun daga lokacin, jama'a a wasu kasashen Afrika Kudu da sahara sun yi ta fatan samun irin wannan sauyi a kasashensu.

Shin ko kuna ganin akwai bukatar wata guguwar sauyin a irin wadannan kasashen na kudu da sahara? Ta yaya za a karfafa demokradiyya a Afrika? Wasu ke nan daga cikin abubuwan da muka tattauna a shirinmu na Ra'ayi Riga na wannan makon.

Multimedia

bbc.co.uk navigation

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.