|
Hukumar kula da wasan kwallon kafa ta duniya wato FIFA tace kawo yanzu ta gamsu da yadda Najeriya ke daukar bakoncin gasar
kwallon kafa ta matasa 'yan kasa da shekaru goma sha bakwai.
A wani taron manema labarai da hukumar ta kira a Abuja, Matamakin Shugaban Hukumar Mista Jack Warner ya ce Najeriya ta taka
rawar gani a wasanin zagaye na farko da aka kamalla , a yayinda kuma ake tunkarar wasanin zagaye na biyu.
Kafin a fara gasar sai da hukumar ta FIFA tayi barazanar dauke gasar daga Najeriya saboda kasa cika wasu sharudan da aka gindaya.
|